Guguwar Sauyi na cigaba da kadawa a Jahar Kebbi
Daga : Sani Mohammed
Tun bayan ficewan tsohon ministan shari'a Abubakar Malami SAN daga jammi'ar APC zuwa jami'ar ADC guguwan sauyi ke cigaba da kadawa da diban manyan Yan siyasa a jahar Kebbi da fadin Najeriya.
Wannan yana kara tabbatar da cewa Abubakar Malami SAN jigo a Jahar Kebbi da fadin Arewa da kuma Kasa baki daya duba da irin rawan ya taka a baya wajen kafa ita kanta Jammi'ar APC mai mulki da kuma nasaran shekaru takwas da suka wuce.
Yanayin siyasar Jihar Kebbi ya girgiza sosai a ranar Talata, bayan sauya sheka da Hon. Nasir Mohammad Dan-Umma ya yi daga jam’iyyar All Progressives Congress (APC) zuwa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), bayan wata muhimmiyar ganawa a bayan fage da tsohon Ministan Shari’a kuma Lauyan Gwamnatin Tarayya, Abubakar Malami (SAN), a Abuja.
Dan-Umma, wanda ya wakilci Karamar Hukumar Argungu a Majalisar Dokokin Jihar Kebbi daga 2015 zuwa 2023 kuma a halin yanzu yana matsayin Mai Bai wa Gwamna Nasir Idris (Kauran Gwandu) Shawara ta Musamman, ya dauki wannan matakin ne bayan wata ganawa ta sirri da Malami da wasu ‘yan siyasa na kusa da shi.
Cikin wadanda suka halarci ganawar ta Abuja akwai abokan amana na Malami — Dr. Hon. Shehu Mohammed Koko, Dr. Sule-Iko Sadeeq S. Sami, da Hon. Yakubu Birnin-Tudu — lamarin da ya nuna cewa sauya shekar ba kawai matsaya ce ta mutum daya ba, sai da hadin gwiwa da tsara sabon salo na siyasa da zai iya kawo canje-canje masu zurfi ga APC a Kebbi.
Sauya shekar Dan-Umma na kara karfin gwiwar ADC, wacce ke samun karbuwa sosai a yankin Arewa maso Yamma. Tunaninsa na siyasa a matakin tushe, tsarinsa na siyasa da kuma gogewarsa mai tsawo a gwamnati sun kara wa ADC karfi da amincewar jama’a a sabuwar tafiyar siyasa a Kebbi.
A bangaren APC kuwa, ficewar tasa babban gibi ne, wanda ke bayyana yadda rabuwar kai da rashin jin dadi ke yawaita a cikin jam’iyyar mai mulki.
Majiyoyi daga cikin gwamnati sun tabbatar da cewa wasu daga cikin masu rike da mukaman gwamnati da na siyasa suna kokarin tuntubar Malami domin “kulla yarjejeniya”, yayin da tattaunawa ke ci gaba da gudana a boye. Sauya shekar Dan-Umma ta bude kofar sauye-sauyen siyasa, kuma ana sa ran wasu fitattun ‘yan siyasa za su biyo bayansa a makonni masu zuwa.
Comments
Post a Comment